A cewar rahoton Ofishin Yada Labaran Hauza, sakon godiyar Ayatullah A'arafi ga al'ummar Iran saboda gagarumin tattakin ranar 22 ga watan Bahman 1404 shi ne kamar haka:
Da sunan Allah mai rahama mai jin kai
Iskar rahamar Ubangiji da kishin ƙasa sun mayar da tattakin 22 ga watan Bahman na shekarar 1404 (11/02/2026) ya zama wani babban abin mamaki da alfahari a tarihin Iran da Musulunci. Wannan ya ƙara ɗaukaka tutar 'yanci da Jamhuriyar Musulunci da kuma gwagwarmaya da mulkin mallaka da zalunci a duniya. Muna gode wa Allah, kuma muna girmama wannan babban mataki na al'ummar Iran, musamman matasa masu neman sauyi da wayewa. Wannan karsashi da aka gani daga ƙauyuka har zuwa manyan birane, musamman a Tehran da Qom, abu ne da ya kamata a yaba masa kwarai da gaske.
A bayyane yake cewa wannan kwarjini na Musulunci da Iran zai sa makiya masu ƙeta ja da baya, sannan zai ƙarfafa gwiwar raunana da masu neman adalci a duniya. Sai dai kuma, wannan babban taron haɗin kai ya sanya babban nauyi a wuyanmu da sauran jami'ai.
Kyautata fahimtar duniya da al'umma, musamman matasa, da ƙarfafa alaƙa da su, da kuma fito da sabbin dabarun bayyana nasarorin Juyin Juya Hali da fuskantar girman kai na duniya (Imperialism), duka suna cikin ayyukan da suka rataya a wuyan hukumomin zartarwa, na shari'a, da na al'adu.
Sakon al'umma shi ne tsayuwa kan manufofin Musulunci da shahidai, da biyayya ga Jagora, da kuma neman jami'ai su ninka ƙoƙarinsu wajen magance matsalolin abinci, rayuwa, da al'adu. Muna fatan hukumomi za su fito da sabbin hanyoyi na ci gaba da warware matsalolin mutane.
Tsira da aminci su tabbata ga fiyayyen halitta, da shahidai madaukaka, da jagoran shahidai (Imam Khomeini), da kuma daukacin al'ummar Iran.
Ali Reza A'arafi
Your Comment